WHO Ta Ayyana Bullar Ebola a Congo a Matsayin Barazana ga Lafiyar Al’umma ta Duniya

WHO Ta Ayyana Bullar Ebola a Congo a Matsayin Barazana ga Lafiyar Al’umma ta Duniya

Daga Edita

Hukumar Lafiya ta Duniya, World Health Organization, ta ayyana ɓullar cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokiraɗiyyar Congo a matsayin babbar barazana ga lafiyar al’umma da ta shafi duniya baki ɗaya, bayan da cutar ta yi sanadiyyar mutuwar sama da mutane 80.

Matakin ya biyo bayan gargaɗin da hukumomin lafiya suka bayar cewa har yanzu babu wani ingantaccen rigakafi ko magani da aka amince da shi domin yaƙar wannan sabon nau’in cutar.

A cikin wani rahoto da Africa Centres for Disease Control and Prevention ta fitar, an bayyana cewa an samu mutum 88 da suka rasu, yayin da ake zargin wasu mutum 336 sun kamu da wannan cuta mai saurin yaɗuwa, wadda ke haddasa zubar jini ta hanci da baki.

Hukumar World Health Organization ta sanar a safiyar Lahadi cewa nau’in Ebola da aka gano mai suna “Bundibugyo” ya kai matsayin da ke barazana ga lafiyar al’umma a matakin duniya.

Hakazalika, ƙungiyar agajin likitoci ta Médecins Sans Frontières ta bayyana shirinta na ƙaddamar da manyan ayyukan bincike da bayar da agajin gaggawa domin dakile yaɗuwar cutar.

Ƙungiyar ta bayyana cewa saurin yaɗuwar cutar abin damuwa ne matuƙa, lamarin da ya yi daidai da gargaɗin da hukumomin gwamnati suka bayar kan hatsarin da cutar ke haifarwa.

Related Articles

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Stay Connected

0FansLike
0FollowersFollow
0SubscribersSubscribe
- Advertisement -spot_img

Latest Articles