19.8 C
Kano
Tuesday, January 27, 2026

Kungiyar Matasan Najeriya reshen Karamar Hukumar  Shanono ta zabi sababbin shugabanni


Kungiyar Matasan Najeriya reshen Karamar Hukumar  Shanono ta zabi sababbin shugabanni don gudanar da harkokinta na tsawon shekaru uku masu zuwa. 


Wadanda aka zaba sun hada da Auwalu Lawan Sani a matsayin Shugaba, Aliyu Salisu Lawan Mataimakin Shugaba, Abba Usman Ahmed a matsayin Ma’ajin Kudi, da Sirajo Garba a matsayin Jami’in Hulda da Jama’a. 


Sauran su ne Anas Hudu Leni Mataimakin Sakatare, Abdulmalik Adam Sakataren Kudi, da Mika’il M Sale Akawu, yayin da Wasila Lawan ta zama Shugabar Mata. 

Bayan zaben, sabon shugaban, Auwalu Lawan Sani, ya yi godiya ga dukkan mambobin saboda amincewar da suka yi masa tare da yin alkawarin yin aiki tuƙuru don samun nasara. 

Shugaban kungiyar, Alh. Abubakar Barau, wanda Shugaban Sashen Ci Gaban Al’umma, Alh. Gambo Isyaku Gwarzo ya wakilta, ya yi kira ga sababbin shugabannin su kasance jakadu nagari na yankin a kowane lokaci. 


Ya kuma ba su shawarar su kasance masu himma wajen kula da walwalan matasa a  Shanono. 


Hafsat Garba 
Jami’ar Yaɗa Labarai Ta Karamar hukumar  Shanono 

Related Articles

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Stay Connected

0FansLike
0FollowersFollow
0SubscribersSubscribe
- Advertisement -spot_img

Latest Articles